- Sam Nda Isaiah yayi takarar shugaban kasa a 2015
- Dan jaridar ya tasa PDP a gaba a da
- Ya lissafta abubuwa 5 da ya kamata shugaba Buhari yayi maza-maza da ya dawo
Babban jigo a jam'iyyar APC kuma mai kokarin gyarawa gwamnatoci zama, Mista Sam Nda Isaiah, ya zayyana abebade 5 da ke da matukar muhimmanci ga gwamnatin shugaba Buhari, da zarar ya tako gida Najeriya.
Muhimman abebade biyar da ke matukar jiran shugaba Buhari ya zo ta kansu da ya dawo
Shekarar nan dai shugaban bayyi wani aiki ba, amma ya mika wa farfesa Osinbajo ragamar mulki, sai dai kuma kash, ba kowanne abu ne doka ta bari Yemi Osinbajon yayi ba, dole sai Buharin da kansa, musamman ganin ba'a bashi sunan mukaddashi ba a hukumance, sai dai mai iyar da tsarin gwamnati.
Ga abubuwan da Sam Nda ya fayyace kamar haka:
1. Sake Ministoci
2. Duba rahoto kan cin hanci a gwamnatinsa da daukar kwakkwaran mataki, musamman batun su kudin NIA a Legas da na Babachir David Lawal
DUBA WANNAN: Bankin Lamuni na duniya IMF ya baiwa Najeriya rahoton sa kan farfadowar tattalin arziki
3. Cike guraben gwamnatoci da a baya ya sauke shuwagabanninsu, wadanda har yanzu ba'a nada ba
4. Sake hade kan 'yan Najeriya, saboda karin zaafan kalamai daga kabilu da bangarorin kasar.
5. Cika alkawurran jam'iyyarsa ta APC wadanda ya dauka shekaru uku da suka wuce.
Ya zuwa yanzu dai ba'a san ranar dawowar shugaba Buhari ba, gashi kuma shekarar zaben 2019 na kara karatowa.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
We appreciate you for reading Teeloadeders, but we think it will be better you like our facebook fanpage and also follow us on twitter below.
Title :
Muhimman ababe 5 da ke matukar jiran shugaba Buhari ya zo ta kansu da ya dawo - Sam Nda Isaiah
Description : - Sam Nda Isaiah yayi takarar shugaban kasa a 2015 - Dan jaridar ya tasa PDP a gaba a da - Ya lissafta abubuwa 5 da ya kamata shugaba Buhari...
Rating :
5