Gwamnatin jihar Kebbi ta kammala shirin fara aikawa da akuyoyi 2000 a kowace rana zuwa kasar Saudiya cikin wata hadin gwiwa data shiga tare da bankin musulunci na Ja’iz.
Kwamishinan kasafin kudi da tsare tsare na jihar, Alhaji Jailani Muhammad Yauri ne ya bayyana haka yayin dayake ganawa da yan jaridu a karshen makon data gabata, kamar yadda NAIJ.com ta ruwaito.
KU KARANTA: Zandoro: an gano mutumin da yafi kowanne ɗan Najeriya tsayi (Hotuna)
Kwamishinan ya kara da cewa jihar sa na kokarin shirya wata alakar kasuwanci tare da kasashen Nijar da Bini, da kuma jihohin Sakkwato da Zamfara da nufin habba tattalin arzikin dukkanin bangarorin.
Akuyoyi
“Mun amince tsakanin kwamishinan
kasafin kudi na Zamfara dana Sakkwato cewa zamu tsara wata alakar kasuwanci a tsakaninmu musamman akan shinkafa da sauran kayan amfanin noma wanda muke sa ran hakan zai inganta kasuwancin mu tare da samar mana da kudaden shiga.” Inji Alhaji Jailani.
Daga karshe Kwamishinan ya koka kan rashin ingantaccen tsarin shirya kasafin kudi mai hangen nesa, tare da karancin kwararru da zasu tafiyar da tsarin.
We appreciate you for reading Teeloadeders, but we think it will be better you like our facebook fanpage and also follow us on twitter below.
Title :
Bunƙasa tattalin arziki: Jihar Kebbi zata fitar da Akuyoyi 2000 duk rana zuwa Saudiya
Description : Gwamnatin jihar Kebbi ta kammala shirin fara aikawa da akuyoyi 2000 a kowace rana zuwa kasar Saudiya cikin wata hadin gwiwa data shiga tar...
Rating :
5